SUN FARA GIRGIZA!
Rundunar ‘yan sanda ta fitar da sakon gaggawa a ma’aikatar — ta na neman a rufe bakin duk wanda ke magana akan zaluncin fansho.
Bayan shekaru 35 na wahala, mutane suna karɓar Naira miliyan 2. Bayan an ƙwace musu dukiyarsu a cikin tsarin PENCOM — yanzu gwamnati da jagororin ’yan sanda na son su yi shiru?
To ga amsar mu:
✊🏽BA ZAMU YI SHIRU BA.
✊🏽BA ZAMU MU YARDA DA YAUDARA BA.
✊🏽BA ZAMU DAKATA BA.
Rundunar ta yarda da ta yi laifi — ta furta da bakinta cewa akwai matsala, har tana cewa “za a yi bincike.” Binciken me? Me ya fi bayyana fiye da miliyoyin da aka sace wa talakawan jami’ai?
Nhàm chán
Bài đăng này đã nhận được nhiều phản hồi từ người dùng vì nội dung đơn điệu và lặp đi lặp lại quá mức.